cookie

We use cookies to improve your browsing experience. By clicking «Accept all», you agree to the use of cookies.

avatar

تربية الأولاد لشيخة رقية

Mun bude wannan channel din ne don ilimantarwa,fadakarwa, tunasarwa,da kuma yada Karatuttukan malaman sunnah.

Show more
Nigeria5 678The language is not specifiedReligion & Spirituality76 229
Advertising posts
950
Subscribers
-124 hours
+87 days
+4630 days

Data loading in progress...

Subscriber growth rate

Data loading in progress...

4.47 MB
4.51 MB
3.55 MB
Show all...
تربية الأولاد لشيخة رقية

Mun bude wannan channel din ne don ilimantarwa,fadakarwa, tunasarwa,da kuma yada Karatuttukan malaman sunnah.

NA JI BA NA SON ABOKIN ZAMANA (3) ! Mataki na farko shine: Ka yi imani da cewa komai naka a kan kaddara yake gudana, don haka kai ma din kaddararka ce ka zauna tare da wanda ba ka so, watakila zuwa wani lokaci, ko kuma har karshen rayuwarka. Na 2. Ka yi kokarin lalubo dalilan da suka canza halin wanda da kake so, har hakan ya juye izuwa kiyaiya, ka kuma gyara naka kurakuren domin inganta rayuwar gaba. Na 3. Ka yawaita yin azkar da salatin Annabi (saw) da adduoi da nufin Allah ya zaba maka mafi alkhairi. Na 4. Ka rinka tashi a karshen dare, kana yin sallolin nafila, kana rokon Allah a cikin sujjada ka rinka fada masa damuwarka, ka kuma nemi ya yaye maka ita. Na 5. Ka nisanci bin son zuciyarka, ka nemi shiryarwa daga ubangijinka, masanin gaibu. Na 6. Ka guji yanke hukunci a cikin halin fushi, ka rinka bari sai bayan ka huce, hankalinka ya dawo jikinka tukuna. Na 7. Ka rinka yawaita neman tsarin Allah daga sharrin shaidanu na aljanu da mutane, a duk lokacin da ka samu kanka cikin damuwa. Na 8. Ka rinka tuno lokacin da kuke zaman lafiya da abokin zaman naka, ka tuno kyawawan halayensa na baya, ka kuma rinka yaba masa a kansu. Na 9. Ka rinka tuna cewa; duk damuwar da musulmi ya shiga, ana kankare masa zununbansa ne a sakamakon hakan. Na 10. Ka rinka yin aiki da nasihohin malamai da sauran mutanen kirki magabata da na zamanin da kake rayuwa. Na 11. Ka rage abokan shawara, domin ba ko wane makusancinka ne yake son ka da alkhairi ba, don haka ka zamo mai shawartar mutanen kirki, masu kaifin hankali da hangen nesa da sanin ya kamata. Na 12. Ka sani cewa; idan ka rabu da abokin zamanka, ba fa dole ne ka samu wanda ya kai nagartarsa ba, don haka maimakon ka rinka rokon rabuwa, gara ka bayar da zabi ga Allah, domin shine masanin abin da ya fi. A gwada aiwatar da wadannan shawarwari, domin ganin kyakkyawan sakamakon da za su bayar, insha`allahu ! Dr Salim Saminu Madabo (Abu Na'ila)
Show all...
﷽ I raise my hands in Prayers for your wishes to be granted, your Ibadat to be accepted and your sins to be forgiven.May Allah (SWT) multiply His blessings on you, your parents and your entire family.Ameen. *Jumu'at Mubarak Good Morning 🥂 @KZ Collectiongyale-kn
Show all...
Show all...
تربية الأولاد لشيخة رقية

Mun bude wannan channel din ne don ilimantarwa,fadakarwa, tunasarwa,da kuma yada Karatuttukan malaman sunnah.

l. Masallacin Juma’a Na Sabilus Sa’adah, Dorayi Babba Yamadawa, kusa da Gidan Dagaci. m. Masallacin Ahmad Bin Hambal, Yamadawa, kan titin AFCO. n. Koren Masallaci, Layin OA. o. masallacin gidan liman rafin dannana dorayi babba p. masallacin gidan malam Awaisu saidu q. Masallacin juma’ah na janbulo 2nd gate r. Masallacin MANARUL Quran 3rd gate janbulo Malakai da suka sa hannu a kan wannan takarda sun hada da: 1. Sheikh Muhammad bin Usman 2. Sheikh Dr. Umar Ibrahim Indabawa 3. Sheikh Lawan Abubakar Triump 4. Sheikh Muazzam Sulaiman Khalid 5. Sheikh Abdulkadir Ismail Kabara 6. Sheikh Yahaya Shehu Maimota 7. Sheikh Khamis Nasidi 8. Sheikh Dr. AliYunus 9. Sheikh Barista Ishaq Adam 10. Sheikh Shehu Mansur 11. Sheikh Dr. Mujtaba Ibrahim Abubakar Ramadan 12. Malam Dr. Salim Saminu Madabo Da sauran malamai da aka takaita a ambato don laakari da takaitawa
Show all...
Bismillahir Rahmanir Rahim Wa sallahu ala nabiyyina Muhammadin wa Alihi Wa Sallam KANO ULAMA FORUM A madadin daidaikun malamai na Jahar Kano da suke wanna shiyya: 1. Muna yi wa Allah Madaukaki godiya tare da mika komai namu zuwa gare shi, a duk yanayin da muka samu kanmu, don shi Ya halicce mu, Ya ba mu lafiya, Ya sanya muka zamo Musulmi. 2. Hakika jarrabawa da ibtila’i tsari ne da Sunnar Allah a cikin Rayuwa: Allah yana cewa: ((Kuma wallahi za Mu jarrabe ku da wani abin tsoro da yunwa da tawayar dukiyoyi da rayuka da 'ya'yan itatuwa. Kuma ka yi albishir ga masu haquri. 156- (Su ne) waxanda idan musiba ta same su, sai su ce: Mu mallakin Allah ne, kuma gare Shi za mu koma)). 3. Saboda haka muna fada muna dada nanata abin da Allah (SWT) da Manzon Allah (SAW) ya koyar da mu. (Inna LIllahi Wa Innan Ilaihi Raji’un). Allahumma Ajjurna fi MUsibatina, Wa Akhluf lana khairan minha). 4. Hakika abin da ya sami ‘yanuwanmu a Borno na ambaliya, gaba dayanmu ya samu, kuma dukkanmu mun shiga damuwa da damuwarsu, mun yi kukan zuci da kukansu. 5. A irin wannan yanayi Allah (SWT) Ya daura mana a matsayinmu na Musulmi masu koyar da al’umma addini, mu yi alhini, mu jajanta, mu yi addu’a, mu nema musu mafita, ko mu sassauta musu damuwa da suka shiga. 6. Hakika lokaci ne da ya wajaba mu mika hannun taimako, mu kai dauki, mu yi kira a masallatai da majalisai, mu tuntubi masu iko da su kai musu dauki na gaggabawa. 7. Hakika wannan azure mai albarka ya tanadi wurare da za a karbi agaji (na tufafi, abinci, ko kudi, da duk wani abu da ake da bukata na gida ne ko na gyara ne, cikin wanda za a ka iya saye, ko kake da shi a cikin shirgin gidanka mai amfani) don mikawa cikin gaggata ga wadannan yanuwa namu da Allah (SWT) cikin ludufinsa ya kaddara musu wannan. 8. Wurare da za a kai wadannan taimakon za a rattaba su a kasan wannan takarda. 9. Muna kira ga shuwagabanni na wancan shiyya, da duk gwamnonin Arewa da su kai agaji da gudun mawa, ba don komai ba, don kada mu bar su ga hannun kuraye, wadanda ba za su yi wata-wata ba wajen mika musu da hannun dama, ya janye su zuwa muguwar akida ta bangaren hagu. 10. Ka sani danuwa Musulmi, wannan aikin da ka yi gado ne daga wajen MasoyinKa Annabi Muhammadu (SAW), sannan ceto ne na yanuwanka kada a wafce su zuwa ‘Ashabus Shimali’, taimakonka zai iya zamowa dalili na kare Musulmi daga barin addininsa da za a iya yaudararsa da agaji duba da halin da yake ciki 11. Muna kira ga masu wadata da hannu da shuni, cikin abin da suka yi a baya na taimakawa a wannan gari a lokacin da aka samu IDP, wanda aka rasa Musulmai da za a su kai musu agaji kuka kai, a yau ma ku zamo cikin ayarin farko na ceton ‘yan uwanku (da magunguna, da barguna, da atamfofi ko yaduka, da duk abin da Allah Ya howace muku). 12 Wannan Account Number ne don ba da gudummawa gare su, abin da aka yi don Allah ba ya kadan ba ya yawa, kuma ita sadaka maganin musiba ce. 1. NUSAID Humanitarian Initiative Acc No. 000 3606 573 2. Muassatu Albir Charitable Foundation Acc No. 000295730 JAIZ Bank Or Acc. No. 2142516137 UBA Bank * Contact No: 08079587630 08087004060 13. Wadannan gurare ne da za a karbi taimakon kaya ko abin taimako don isarwa ga wadannan yanuwa namu, ka zamo mai bayarwa, ko mai karfafa a bayar, ko mai yada sanarwar a taimaka, sai mu yi tarayya baki daya cikin lada. a. Masallacin Darul Hadith Tudun Yola, Kano b. Masallacin Usman bin Affan da ke GAdon kaya, Kano c. Masallacin Juma’a na Triump da ke Fagge, Kano d. Masjidul Faruk da ke Unguwa uku, Kano e. Masallacin Ihya’us Sunna da ke Gwammaja Kano f. Masallacin Hasan Ibnu Ali da ke Dorayi Babba, Kano g.Masjid Sahaba, Kundila, Kano h. Masallacin Dorayi.Babba i. Masallacin Juma’a na shababul Qur’ani J. Masallacin JTI Bajallabe, k. Masallacin Mu’azu Bin Jabal, Janbulo Layin OC kusa da Gidan Mai Unguwa.
Show all...
4.15 MB
4.53 MB
1.83 MB
Show all...
تربية الأولاد لشيخة رقية

Mun bude wannan channel din ne don ilimantarwa,fadakarwa, tunasarwa,da kuma yada Karatuttukan malaman sunnah.

Choose a Different Plan

Your current plan allows analytics for only 5 channels. To get more, please choose a different plan.